Kamar dai yadda ya saba sanata mai wakiltar kananin hukomomi sha biyu (12) na yankin Katsina ta arewa (Daura Zone) ya bada taimakon naira dubu dari hudu da hamsin da ukku domin kai wani mara lafiya Mai suna malam Abdulbasiru asibiti don yimashi magani.
Hakan ya biyo bayan wani rubutu da Faisal Shaaibu yayi a dandalin sada zumunta na facebook akan wannan mara lafiya inda shi kuma baiyi wata-wata ba sai ya amsa da a hanzarta kai mara lafiyan asibiti.
Allah ya saka da alkhairi Sen Ahmad Babba Kaita ya cigaba da yimaka jagoranci na alkhairi ameen.
No comments:
Post a Comment